Rundunar sojin saman Nijeriya ta karyata batun kai wa masu maulidi hari

top-news

Rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta cewa tana da hannu a harin da aka kai ta sama a karamar hukumar Tudun Biriin Igabi a jihar Kaduna wanda rahotanni suka ce mutane kusan 30 ne suka mutu a yayin taron Mauludin Annabi (SAWW) da aka yi a daren Lahadi.

Gwamnatin jihar Kaduna ta shaida wa manema labarai cewa gwamnati za ta yi wa manema labarai jawabi a kan lamarin a gidan gwamnati a yau Litinin.

Sai dai NAF a wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin ta ce ba ta gudanar da wani samame a Kaduna ba a cikin sa'o'i 24 da suka gabata.

“Labarin da ake yadawa na cewa jiragen sojojin saman Nijeriya (NAF) sun kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a Kaduna karya ne. Muna sanar da ku cewa NAF ba ta gudanar da wani samame a jihar Kaduna da kewaye ba a cikin awanni 24 da suka gabata.

“Har ila yau, muna son ku lura cewa NAF ba ita ce kawai rundunar da ke aiki da jiragen yaki marasa matuka ba a yankin Arewa maso yammacin Nijeriya,” in ji NAF a cikin sanarwar da Air Commodore Edward Gabkwet, Daraktan Hulda da Jama'a da Yada Labarai ya sanyawa hannu.

Sanarwar ta kara da cewa, “Yana da muhimmanci a tabbatar da cewa kafofin yada labarai suna hanzarin wajen buga rahotannin da ba a tabbatar da su ba.

Ammar Muhammad Rajab @Katsina Times 

NNPC Advert